IQNA

‘Yar tseren kasar Holland tare da 'yan wasa musulmi sanye da gyale

18:47 - August 14, 2024
Lambar Labari: 3491697
IQNA - 'Yar tseren kasar Holland da ta lashe lambar zinare a gasar tseren guje-guje da tsalle-tsalle ta Olympics ta sanya hijabin Musulunci a lokacin da ta karbi lambar yabo domin nuna rashin amincewarta da manufofin kyamar Musulunci na kasashen Turai.

Zakarar gasar Olympics ta kasar Holand, ta je filin wasa ne sanye da hijabi a lokacin da ta yi nasara tare da lashe lambar zinare a tseren gudun fanfalaki a ranar karshe ta gasar Olympics ta birnin Paris.

Da aka yi nazarin hotunan wannan ‘yar wasa ‘yar asalin kasar Habasha a shafin Instagram, ta bayyana cewa ba ta cikin 'yan wasan da suka sala lullubi kuma ta halarci gasar ba tare da lullubi ba. Sai dai ta sanya hijabi a lokacin da ta karbi lambar yabo ta nuna rashin amincewarta da manufofin kin jini da ake nuna  wa 'yan wasa musulmi mata.

Masu fafutuka a shafukan sada zumunta sun sanar da cewa, Sifan Hassan ta yi niyyar aikewa da sako  ga masu hana mata saka lullubi, kuma ta yi nasarar zama wata alama a ranar karshe ta karbar lambar zinare da aka raba a gasar Olympics.

Bayan lashe zinare a tseren mita 5,000 da 10,000 da tagulla a tseren mita 1,500 a Tokyo sannan ta samu tagulla a tseren mita 5,10,000 a birnin Paris, wannan 'yar kasar Holland ta kawo adadin lambobin yabo na Olympics guda 6.

 

4231671

 

 

captcha