Dr. Haider al-Ramahi, wani manazarci Iraqi, ya rubuta a cikin wani rubutu mai suna "Ziyarar Arbaeen daga mahangar diflomasiyyar jama'a" da aka buga a shafin intanet na Baratha News:
Tun bayan waki'ar Karbala, lamarin ziyarar arbaeen na imam Husaini ta wuce muhimman sauye-sauyen siyasa a yankin, musamman ma yankunan Iraki, Sham da kasashen Larabawa. Kuma duk da cewa daukar fansar zub da jinin Imam Husaini (AS) ya tabbata a hannun Mukhtar Thaghafi da wadanda suke tare da shi sun share masa hanya, amma yunkurin Imam Husaini (a.s.) ya yi kamar ya fi karfin jini ko daukar fansa a kan masu laifin wannan lamari.
Yunkurin Imam Husaini (a.s.) ya taso ne saboda su, musamman a fagen jagorancin musulmi, sauye-sauyen siyasa, 'yanci da tsayin daka kan zaluncin azzalumai, ya dauki wani salo na daban. Domin kuwa wadannan ka’idoji da ra’ayoyi sun fara girma har sai da suka kai wani mataki da ya zama tamkar kaya a idanun shuwagabanni azzalumai a tsawon tarihi, kuma hakan ya haifar da jarabawa ga mabiya mazhabar ahlul bait a lokuta daban-daban da matsin lamba na siyasa, zamantakewa da tattalin arziki.
Duk mai bibiyar tarihi zai iya fahimtar yadda sarakunan Banu Umayyawa da Abbasiyawa suka tsaya tsayin daka wajen adawa da tsarin Imam Husaini na bin sahihin tafarkin addini na asali kuma na hakika daga manzon Allah (SAW) da yadda suka afkawa mabiya tafarkin ahlul bait.
Haka nan ma mabiyansu sun kasance haka har zuwa wani lokaci, har ta kai ga an tilasta musu gudanar da tarukan nasu a asirce saboda tsoron sarakunan Umayyawa da Abbasiyawa.
Har zuwa intifada na watan Safar a shekara ta 1977 a Iraki, kuma bayan gwamnatin Baath ta kasar ta hana 'yan Shi'a gudanar da zaman makokin Imam Husaini, 'yan Shi'ar Iraki sun fito fili suna adawa da gwamnatin Ba'ath kan irin wannan zalunci da suka fuskanta. Ko da yake wannan boren ya kai ga kashe 'yan Shi'a da dama a karkashin gwamnatin Saddam.
Bayan wadannan abubuwa masu zafi da suka faru a tarihi a kan mabiya mazhabar Shi'a, sai aka yi kuka da lamiri na hankali bayan budeirin wadannan ayyukan a duniya, kuma gaskiya karara tana magana ne kan irin gagarumin ci gaban da aka samu na ziyarar Arba'in tun daga shekara ta 2003 miladiyya, kuma a wannan lokacin, an sami ci gaba idan aka kwatanta da na baya-bayan nan.
Domin kuwa adadin masu ziyarar Arbaeen ya karu daga mutane miliyan 3 a shekara ta 2003 zuwa sama da maziyarata miliyan 22, haka kuma ya karu daga halartar kasashe 3 ko 4 a wannan taro zuwa halartar kusan kasashe 50 ko ma fiye da haka.