A daidai da daren wafatin Annabi Muhammad Mustafa (AS) da kuma shahadar Imam Hassan Mujtabi (a.s) za a gudanar da shirin "Rahmatul Al'amin" wanda cibiyar kula da harkokin kur'ani ta hubbaren Radawi za ta gudanar.
An sadaukar da wannan aiki ne domin karatun suratul Mubaraka Muhammad (s.a.w) tare da bayar da ladarsa ga manzon Allah (SAW) kuma lokacin aiwatar da shi zai kasance ne a ranar Lahadi bayan sallar Magariba da Isha'i.
Za a gudanar da shirin karatun gaba dayan suratu Mubaraka Muhammad a wuri guda a Haramin Radavi, da masallatai da aka zaba a fadin kasar.