Shafin sadarwa na yanar gizo na Al-Khalij Online ya bayyana cewa, tawagar gwamnatin Saudiyyar ta tattauna a taronta na tuntuba da tuntubar juna tsakanin Saudiyya da kasashe abokantaka da kuma ‘yan uwantaka dangane da ci gaban yanki da na kasa da kasa, da fatan samun hadin kai, da hanyoyin tallafa mata a fannoni daban-daban.
Tawagar gwamnatin Saudiyyar ta jaddada aniyar kasar ta Saudiyya kan rawar da take takawa wajen tallafawa kokarin da ake na tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali na kasa da kasa da kuma rage radadin al'ummar da abin ya shafa da mabukata.
Riyadh da Paris sun fitar da sanarwar hadin gwiwa a watan Janairu, biyo bayan ziyarar da shugaban Faransa Emmanuel Macron ya kai Saudiyya, ciki har da gudanar da taron kasa da kasa a watan Yuni domin nuna goyon baya ga kafa kasar Falasdinu.