Ya ce tattaunawar tasu ta mayar da hankali ne kan yadda za a samu taimakekeniya a tsakanin bangarorin biyu dangane da yin nazari kan addinai da kuma karawa juna sani, kuma sun cimma matsaya kan hakan.
Kasashen Iran da kuma Ethiopia dai suna da tsohon tarihi na dangantaka a dukkanin bangarori na al'adu da ilimi da ma kasuwanci, kasantuwar al'ummomin kasashen biyu suna da dadadden tushea tarihi na dubban shekaru.
Dukkanin bangarorin biyu dai sun amince a kan fara yin aiki dangane da yadda za su tsara hanyoyin karuwa da juna, inda Iran za ta rika tura masu bincike zuwa wannan kwaleji domin kara samun bayanai da kuma ilmomi da suka danganci akidun da ake koyarwa a wannan kwaleji.
A nata bangaren kuwa kwalejin za ta rika gudanar da bincike a cibiyoyin kaar Iran kan lamrinadini da kuma al'adu da suka danganci addinin muslunci.