IQNA

Masar Ta Yi Gargadi Kan Yin Amfani Da Kalmar Ta’addancin Musulunci

15:08 - December 05, 2019
Lambar Labari: 3484294
Bangaren kasa da kasa, cibiyar bayar da fatawa a Masar ta yi gargadi kan yin amfani da Kalmar ta’addancin musulunci.

Kamfanin dillancin labaran IQNA, shafin tashar Russia Today ya bayar da rahoton cewa, a jiya babbar cibiyar bayar da fatawa a Masar ta yi gargadi kan yin amfani da Kalmar ta’addancin musulunci tare da bayyana hakan a matsayin wata hanya ta bakanta fuskar musulunci, da aka fara amfani da ita a 2001.

Cibiyar ta ce babu wani abu ta’addancin musuluci domin kuwa addinin musulunci ba addinin ta’addanci ba ne, saboda haka ba abu ne da za a amince da shi ba a ci gab ada yin amfani da wannan kalma dake danganta ayyukan ta’addanci da musulunci.

Darul Ifta Masar ta ce bayan kai harin 11 Satumba a 2001 ne aka fara yin amfani da Kalmar, sai kuma a harin Madrid 2004, da London 200, da Stockholm 2010, da kuma bayan kirkiro Daesh a 2014.

 

3861865

 

https://iqna.ir/fa/news/3861865

captcha