Kasashen Saudiyya, Tunisia, Kuwait, Bahrain, Yemen, Turkiya, Darul Ifta Lebanon, UAE, Qatar, da wakafin Sunni a Iraki, sun sanar da gobe Juma’a 24 ga watan Afirilu a matsayin ranar daya ga watan Ramadan mai alfarma.
Hukumomi a Saudiyya, sun sanar da hango jinjirin watan Ramadana da yammacin ranar Alhamis, wanda ya kawo karshen watan Sha’aban.
Hakan dai ya sanya Juma’a ranar farko ta watan azumin Ramadana a Saudiyya.
Bana dai za’a gudanar da azumin a cikin wani irin yanayi da ba’a taba fuskanta ba sakamakon annobar coronavirus a duniya.
Kafin hakan dama a Saudiiya Babbar majalisar koli ta malamai ta bukaci al'ummar Musulmin duniya a kasashen da ke fama da cutar korona su yi Sallah a gidajensu lokacin watan Azumin Ramadan.
Malaman sun ce: "Ya kamata musulmi su zama abin misali ta hanyar gudanar da addininsu yayin da suke kiyaye matakan kariya da hukumomi suka dauka a kasashen da suke," in ji sanarwar.
Sannan majalisar ta bukaci musulmi su kauracewa duk wani taro a lokacin buda-baki ko sahur a cikin Azumi.