Tashar Alakhbar 24 ta bayar da rahoton cewa, Kamar yadda Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa alihi Sallam ya koyar game da yin sallah a lokacin da aka samu jinkirin damina, a safiyar jiya ne masallata daga sassa daban-daban na kasar Saudiyya suka gudanar da sallar rokon ruwan sama.
A birnin Makkah, an gudanar da sallar rokon ruwan sama a Masallacin Harami, karkashin jagorancin Abdul Rahman bin Abdul Aziz Al-Siddis, babban daraktan Masallacin Harami da Masallacin Annabi.
A cikin hudubar sallar rokon ruwan sama, Abdurrahman Sudais ya yi kira ga mutane da kada su yanke kauna daga rahamar Ubangiji.
A madina, jama'a da dama sun gudanar da sallar rokon ruwan sama a masallacin Annabi bisa ka'idoji na kiwon lafiya da kuma kiyaye tsafta.
Tun da farko dai Sarkin Saudiyya Salman ya bukaci al'ummar kasar da su gudanar da addu’oi a lokacin sallar la'asar a sassa daban-daban na kasar a jiya Litinin.