Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, A cikin jawabin da ya gabatar a wajen taron, Hojjat al-Islam wal-Muslimin Rafi'i ya bayyana iyalan Fatimah a matsayin abin koyi na iyali musulmi inda ya ce: "Tsayar da Allah da sanya shi a gaba a cikin komai da tarbiyyar addini", "Mutunta hakkin dangi". "Sauƙaka lamurra da kamewa da nisantar almubazzaranci, da kyawawan halaye kamar gaskiya, riƙon amana da aminci" da "ƙauna saboda Allah, suna daga cikin halayen Fatima da iyalanta.