IQNA

Taron Majalisin Makokin Shahadar Fatima Zahra (AS) Tare Da Halartar Jagoran Juyi A Iran

19:02 - January 06, 2022
Lambar Labari: 3486788
Tehran (IQNA) An gudanar da zaman makoki na daren shahadar Sayyida Fatemah Zahra, amincin Allah ya tabbata a gare ta, a Hossiniyyar Imam Khumaini tare da halartar jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, A cikin jawabin da ya gabatar a wajen taron, Hojjat al-Islam wal-Muslimin Rafi'i ya bayyana iyalan Fatimah  a matsayin abin koyi na iyali musulmi inda ya ce: "Tsayar da Allah da sanya shi a gaba a cikin komai da tarbiyyar addini", "Mutunta hakkin dangi". "Sauƙaka lamurra da kamewa da nisantar almubazzaranci, da kyawawan halaye kamar gaskiya, riƙon amana da aminci" da "ƙauna saboda Allah, suna daga cikin halayen Fatima da iyalanta.

Shima a wannan taron Malam Mahmoud Karimi ya karanta makoki wafatinta.
 
 
https://iqna.ir/fa/news/4026616
captcha