Taron na jiya talata dai ya sami halattar shugaban kasar Iran, dr Hassan Ruhani, shugaban majalisar dokokin kasar Iran da kuma alkalin alkalan kasar. A jawabinsa wajen bude taron Dr Hassan Ruhani, shugaban kasar Iran ya yi kira ga kasashen musulmi su hada kai, su kuma yi amfani da dimbin arzikin da Al..ya basu don samar da wani sauyi babba a duniya, wanda kuma zai bawa musulmi matsayin da ta dace da su a cikinta.
Shugaban kungiyar majalusun dokokin kasashen musulmi na 8, wanda kuma shi ne shugaban majalisar dokokin kasar Sudan Fatihu Izzuddeen Mansur a cikin jawabinsa a taron na jiya, ya bayyana cewa yana daga cikin manufofin kafa majalisar, samarwa al-ummar Palsdinu yencinta da kuma hana yahudantar da lardin Palasdinu da aka mamaye.
Shugaban majalisar dokokin kasar Iran Dr Alin Larijani, wanda kuma ya karbi jagorancin kungiyar a matsayin shugabanta na 9, ya bukaci hadin kai tsakanin musulmi, don hana makiya ci gaba da jefa gaba da kiyyayya tsakaninsu, da kuma amfani da wasu masu kafirta musulmi don samar da fitinu a tsakaninsu.
A zaman kungiyar ta jiya dai shuwagabannin majalisun dodkoki na kasashen Afganistan, Suriya, Iraqi, Kuwait, Lebanon, Qatar, Niger, Omman, Emarat, Bangladesh, Yemen, Ivory Coast, Azarbajan, Jordan, Malasia da kuma Sudan ne suka gabatar da jawabansu.
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ce ta jagoranci kafa kungiya ta majalisun dokokin kasashen musulmi a shekara 1999 da nufin samar da hadin kai da kuma ya da arzikin da addinin Musulunci yake da shi a bangarorin rayuwar bil’adama daban daban. Za’a kammala taron a yau laraba.