IQNA

An bude taron kungiyar 'yan Baruwamnu akan Palasdinu a yau litinin

20:05 - August 05, 2014
Lambar Labari: 1436334
Bangaren siyasa, An bude taron kungiyar ‘yan ba-ruwanmu anan Tehran domin taimakawa al’ummar Gaza. Taron wanda ya sami halartar ministocin harkokin wajen kasashe mambobi an bude shi ne da jawabin shugaban kasar Iran Dr. Hassan Rauhani.

 Shugaban na jamhuriyar Musulunci ya yi kira da a kawo karshen zubar da jnin al’ummar Palasdinu da h.k. Isra’ila ta ke yi da kuma duake takunkunin da aka kakabawa yankin Gaza.
Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, bugu da kari shugaban kasar  Iran din ya  zargi h.k. Isra’ila da yi wa palasdinawa kisan kiyashi. Shi kuwa ministan harkokin wajen Palasdinu .. ya yi Allah wadai ne da gajiyawar kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya wajen kawo karshen  zubar da jinin al’ummar Gaza.
Ya kuma ci gaba da cewa za su kwankwasa kofar kowace kungiya ta kasa da kasa domin takawa h.k. Isra’ila birki. Bayanin bayan taron ya amince da shawarar da  ministan harkokin wajen kasar Lebanon ya gabatar na kai karar h.k. Isra’ila a gaban kotun manyan laifuka ta kasa da kasa. 
Wannan dais hi ne karo na farko dacwannan kwamiti ya gudanar da zamansa tun bayan da haramyacciyar kasar Isra'ila ta fara kaddamar da hare-haren bayanan a kan fararen hula a yankin Gaza.
1435614

Abubuwan Da Ya Shafa: Teh
captcha