IQNA

'Yan Ta'addan da Suka Kai Hari A kan taron Ashura A Ihsa Sun Cancanci Ukuba

21:12 - November 05, 2014
Lambar Labari: 1470514
Bangaren kasa da kasa, kungiyar malaman addinin muslunci a kasar saudiyya ta bayyana cewa mutaen ad suka kai harin garin Ihsa a kan masu tarukan Ashura sun cancanci babbar ukuba domin sanya hakan ya zama abin lura gas aura.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa cewa jami’an tsaron Sudiyya sun sanar da kamo mutanen da su ka kai harin ta’addanci akan ‘yan shiyar da ke juyayin Ashura a wani kauye da ke gabacin kasar.

Tashar telbijin din arabiyya ta Saudiyya ta ambato majiyar tsaron kasar na cewa; an kame mutane tara wadanda su ka kai harin a yankin Ihsaa da ke gabacin Saudiyya a daren jiya wanda ya yi sanadin shahadar mutane 7 da jikkata wasu, mafi yawancinsu kananan yara. Bugu da kari majiyar ta ce; mutanen sun shirya kai wasu hare-haren a cikin garuruwan Khubar da Qatif da ke gabacin kasar inda mafi yawancin mutanensa ‘yan shi’a ne.

Harin na jiya ya zo ne dai a lokacin da ake rayuwa cikin zullumi a  gabacin Saudiyya din, bayan yanke hukumcin kasa da wata kotun kasar ta yi wa daya daga cikin fitattun malaman shi’ar kasar Sheih Nimr.


1470182

Abubuwan Da Ya Shafa: ashura
captcha