IQNA

Mutane 25 Ne Suka Kara A Ranar Farko Ta Gasar Karatun Kur'ani Mai Tsarki A Saudiyyah

21:34 - November 17, 2014
Lambar Labari: 1474382
Bangaren kasa da kasa, an bude gasar ne a jiya inda a bangaren safe mutane 11 suka fara karawa da juna, sai kuma da yamma mutane 14 suka kara.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na jaridar Alwatan ta kasar saudiyya cewa, bayan bude gasar da safe a jiya makaranta daga kasashen daban-daban sun kara, da suka hada da Bahrain, Chad, Gambia, Pakistan, Libya, Moroco, Niger, kamaru, Mauritania, Philipines da kuma Algeria.

Sai kuma da yamma da aka gudanar da bangare na biyu a rana ta farko, kasashen da suka kara da juna a yammacin na jiya sun hada da Tunisia, Indonisia, Senegal, Tajikistan, Nigeria, Kamaru, Myanmar, Bahrain, Bosni da kuma Afirka ta kudu.

Gasar dai tana samun halartar makaranta da mahardata kimanin 138 daga kasashen duniya 59 kamar dai yadda masu tsara gasar suka sanar, wanda kuma shi ne karo na talatin da shida da ake gudanar da irin wannan gasa a ta kasa da kasa a Saudiyyah.

Ana gudanar da ita e a bangaren karatun kur'ani da harda a bangaren kur'ani baki daya, sai kuma bangaren izihi 15 da kuma izihi 5, wada dukkanin bangarorin ana karawa a cikinsu.

1473666

Abubuwan Da Ya Shafa: gasa
captcha