Kamfanin da ke kula da harkokin harkokin kur'ani a nan Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna bayan ya nakalto daga majiyar watsa labarai ta Times of India ya watsa rahoton cewa; a daga ranar hhudu zuwa shidda ga watan Shahrivar na wannan shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin da tara hijira shamsiya za a fara gudanar da gasar karatun kur'ani mai girma a kasar Indiya a albarkacin watan Ramadana watan da a cikinsa aka sabkar da kur'ani. Har ila yau ya kara da cewa kimanin mahardata dari biyu da hamsin da kuma makaranta daga fadin lardin Maharashtara za su fafata da juna dad akin taro na Dakin Hajji na birnin Bombai kuma kungiyar mai zaman kanta ce ta shirya da kuma za a bawa mutane goma dad a suka zo na farko kyau ta musamman.
638531