IQNA

Hukumar Tuntuba Ta Musulmi Na Kokarin Ganin Palasdinu Ta Zama Mamba A Yunesco

12:45 - November 01, 2011
Lambar Labari: 2215700
Bangaren kasa da kasa: Ikmalul Dine Ihsan Uglo babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi a wata ganawa da yayi da wakilan kasashe mambobi a cikin wannan kungiya da kuma wadanda ba mambobi ba a cikinsu a birnin Paris fadar mulkin kasar Faransa suna bin diddigin ganin Palsdinu ta zama mamba a cikin hukumar al'adu ta majalisar dinkin duniya Unesko.



Kamfanin dillancin labarai na Ikna da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar musulunci ta Iran ne ya watsa rahoton cewa: Ikmalul Dine Ihsan Uglo babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi a wata ganawa da yayi da wakilan kasashe mambobi a cikin wannan kungiya da kuma wadanda ba mambobi ba a cikinsu a birnin Paris fadar mulkin kasar Faransa suna bin diddigin ganin Palsdinu ta zama mamba a cikin hukumar al'adu ta majalisar dinkin duniya Unesko.Kafin haka dai kasashe da kungiyoyi da hukumomi na ciki da na kasa da kasa sun sha yin yunkurin ganin an sanya Palsdinu a cikin wannan kungiya amma hawa kujerar naki da adawa da hakan da kasashen yammaci musamman Amerika ya hana kaiwa ga nasara.

890777

captcha