Bangaren harkokin kur'ani mai girma: cibiyar kula da al'adun jamhuriyar musulunci ta Iran a birnin Delhu No na kasar Indiya a daidai lokaci guda na fara makon hadin kai a tsakanin musulmi ta shirya gasar karatun kur'ani mai girma da harda a fadin kasar ta Indiya daga ranekun sha bakai zuwa sha tara ga watan Bahman na shekara ta dubu daya da dari uku da tis'in hijira shamsiya karkashin sa idon wakilin hukumar kula da al'adun jamhuriyar musulunci ta Iran a wannan kasa.
Kamfanin dillancin labarai na Ikna ne da ke kula da harkokin kur'ani mai girma a nan jamhuriyar musulunci ta Iran ne ya watsa rahoton cewa: cibiyar kula da al'adun jamhuriyar musulunci ta Iran a birnin Delhu No na kasar Indiya a daidai lokaci guda na fara makon hadin kai a tsakanin musulmi ta shirya gasar karatun kur'ani mai girma da harda a fadin kasar ta Indiya daga ranekun sha bakai zuwa sha tara ga watan Bahman na shekara ta dubu daya da dari uku da tis'in hijira shamsiya karkashin sa idon wakilin hukumar kula da al'adun jamhuriyar musulunci ta Iran a wannan kasa. Kimanin makaranta dari daya da talatin da shida day a kumshi mahardata arba'in da biyar da kuma makaranta tamanin da biya da suka fito daga larduna da jahohi daban daban na kasar kama da Delhu,Utariradesh,Bihar,Kashmir,Hariyana,Maharashtara,Andraparadesh,Carkonad ,Tamilnado da Tabtanam suka halarci wannan gasar da fatar Allah ya bawa mai rabo sa'a.
948165