IQNA

Majaloisar Dinkin Duniya Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Daina Rusa Gidajen Palastinawa

23:40 - December 06, 2014
Lambar Labari: 2615760
Bangaren kasa da kasa, majalisar dinkin duniya ta bukaci haramtacciyar kasar Isra’ila da ta daina aikin wuce goda da irin da take yin a rusa gidajen palastinawa ba gaira ba sabar.

Kmafanin dilancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na jaridar Al-sharq ta kasar Saudiyya cewa, a cikin wani bayani da ta fitar majalisar dinkin duniya ta bukaci haramtacciyar kasar Isra’ila da ta dakatar da wuce goda da irin da take yi na rusa gidajen palastinawa a yankuna gabacin quds da sauran yankuna.
Su ma a nasu bangaren Masu rajin kare hakin bil-adama na Majalisar Dinkin Duniya sun bukaci da a dakatar da rusa gidajen Palastinawa cikin gaggawa.   A wani rahoto da hukumar kare hakin bil-adama ta majalisar dinkin duniya ta fiyar a yau ta siffanta rusa gidajen na Palastinawa da Gwamnatin haramcecciyar kasar Isra'ila ke yi a matsayin shelar yaki da Palastinawa da kuma laifukan yaki sannan ta bukaci Hukumomin na haramtacciyar kasar Isra’ila da su tsaida wannan ta'asa cikin gaggawa. 
A makun da ya gabata ne , piraministan haramcecciyar kasar Isra'ila Banjamin Natan yahu ya bada umarnin rusa gidanjen Palastinawa da suke adawa da manufofin Isra'ila.inda a ranar laraban da ta gabata Sojin haramtacciyar kasar Isra’ila suka rusa gidan Shahid AbdulShaludi wanda ya kai hari  da motar sa ga wasu yahudawa a Baitul-mugadas.
A tunanin Natan Yahu yin hakan shi ne dauka fansa ga iyalansa da kuma hana abkuwar irin wannan hari a nan gaba.
2615222

Abubuwan Da Ya Shafa: palestine
captcha