IQNA

23:40 - December 06, 2014
Lambar Labari: 2615760

Majaloisar Dinkin Duniya Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Daina Rusa Gidajen Palastinawa

Bangaren kasa da kasa, majalisar dinkin duniya ta bukaci haramtacciyar kasar Isra’ila da ta daina aikin wuce goda da irin da take yin a rusa gidajen palastinawa ba gaira ba sabar.

Kmafanin dilancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na jaridar Al-sharq ta kasar Saudiyya cewa, a cikin wani bayani da ta fitar majalisar dinkin duniya ta bukaci haramtacciyar kasar Isra’ila da ta dakatar da wuce goda da irin da take yi na rusa gidajen palastinawa a yankuna gabacin quds da sauran yankuna.
Su ma a nasu bangaren Masu rajin kare hakin bil-adama na Majalisar Dinkin Duniya sun bukaci da a dakatar da rusa gidajen Palastinawa cikin gaggawa.   A wani rahoto da hukumar kare hakin bil-adama ta majalisar dinkin duniya ta fiyar a yau ta siffanta rusa gidajen na Palastinawa da Gwamnatin haramcecciyar kasar Isra'ila ke yi a matsayin shelar yaki da Palastinawa da kuma laifukan yaki sannan ta bukaci Hukumomin na haramtacciyar kasar Isra’ila da su tsaida wannan ta'asa cikin gaggawa. 
A makun da ya gabata ne , piraministan haramcecciyar kasar Isra'ila Banjamin Natan yahu ya bada umarnin rusa gidanjen Palastinawa da suke adawa da manufofin Isra'ila.inda a ranar laraban da ta gabata Sojin haramtacciyar kasar Isra’ila suka rusa gidan Shahid AbdulShaludi wanda ya kai hari  da motar sa ga wasu yahudawa a Baitul-mugadas.
A tunanin Natan Yahu yin hakan shi ne dauka fansa ga iyalansa da kuma hana abkuwar irin wannan hari a nan gaba.
2615222

Abubuwan Da Ya Shafa: palestine
captcha