
Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadawa na yanar gizo na tashar PressTV cewa, rikicin da ya faru a jamhuriyar Afirka ta tsakiya yayi sanadiyyar akasarin masallatan kasar an rusa su ko kuma an lalata su, ta yadda kimanin masallatai 436 an rusa 417 a sassa daban-daban na kasar.
A nasa bangaren firayi ministan Jamhuriyar Afirka ta tsakiya ya jaddada cewa babu gudu babu ja da baya wajen aiwatar da shirin da gwamnatinsa ta sanya a gaba na dawo da doka da oda a fadin kasar baki daya, tare da shiga kafar daya da duk wanda ya nemi kawo tarnaki ga wanann shiri.
Firayi ministan na Afirka ta tsakiya Kamun ya bayyana hakan ne a jiya a lokacin da yake gabatar da wani jawabi da gidajen talabijin na kasar suka watsa kai tsaye, inda ya ce tuni gwamnatinsa ta fara aiwatar da dukaknin shirye-shiryenta domin ganin kasar ta farfado daga matsalolin da ta shiga, da hakan ya hada da batun tsaro da kuma habbaka tattalin arziki.
A daren juma'ar da ta gabata ce dai wasu mayakan kungiyar kiristoci suka kai farmaki a wasu unguwanni na mabiya addinin muslunci a cikin birnin Bangui, inda ya sha alwashin kame dukkanin wadanda suke da hannu a cikin wannan lamari domin gurfanar da su a gaban kuliya.