IQNA

Za A Gina Cibiyoyin Kur’ani Guda 30 A Kasasashen Afirka Na Somalia Da Brundi

20:17 - July 01, 2015
Lambar Labari: 3322221
Bangaren kasa da kasa, cibiyoyin gudanar da ayyukan jin kai na kasar Qatar za su gina cibiyoyin hardar kur’ani mai tsarki a kasashen Afirka guda biyu wato Brundi da kuma Somalia.


Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin nsadarwa na yanar gizo na jaridar kasar Qatar da Al-arab cewa, cibiyar RAF ta kasar Qatar tana gudanar da ayyukan jin kai a kasshen Afirka musamman a kasar ta Somalia inda take daukar nauyin ayyukan alhairi musamman ma a cikin watan Ramadan a cikin kasashen,

Daga cikin ayyukan da za su gudanra  halin yanzu har da gina cibiyoyi na koyar da hardar kur’ani mai tsarki guda 30 a cikin wadannan kasashe, inda  ahalin yanzu sun ware kudi har Riyal miliyan 2 da kuma 407 domin gudanar da wannan gagarumin aiki na alkhari.

Masu gudanar da shirin sun ce za a gina wadannan ciyoyi guda 30 ne  acikin wadannan kasashe, tare da bas u dukkanin abubuwan da suke bukata na aiki, za a gida guda 25 a cikin kasar Brundi, sa kuima guda 5 a cikin kasar Somalia.

Kowace daya daga cikin cibiyoyin za ta lakume kudi har riyal dubu 76, kuma hakan kowane daga cikin cibiyoyin zai kwashi dalibai 80 maza da mata domin koyar da su hardar kur’ani mai tsarki.

3322011

Abubuwan Da Ya Shafa: qatar
captcha