Kamfanin dilalncin labaran Iqna ya nakalto daga jaridar Almisriyun da ake bugawa akasar Masar cewa, Muhamamd Albushari shugaban babbar kungiyar musulmin kasar Faransa, ya ce suna kira ga dukkanin musulmi a cikin kasar farasa da am duniya bakidaya, da su yi Allawadai da harin ta’addanci.
Bushari ya ce musulmin da suke zaune a nahiyar turai su ne suka zama ragon layya na ayyukan ta’addancin da ake yi da sunan Musulunci, ya ce ‘yan ta’addan suna bata sunan muslunci.
Musulmin kasar Faransa sun kirayi limamansu da su fito fili su soki lamirin duk wani dan ta’adda, kuma su nisanta addinin muslunci da wadannan mutane da mumman aikin da suke yi da sunan wannan addini mai tsarki.
3454490