
Kamfanin dilalncin labaran iqna ya
habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na cibiyar yada al’adun
muslunci cewa, a lokacin da shugaban kasar Iran Hassan Rauhani yake isa a
birnin Paris na kasar Faransa za a bude wani taro na makon al’adu na Iran a
kasar ta Faransa tare da halartar shugaban, da kuma wasu daga cikin jami’an
kasar ta Iran da kuma na Faransa, inda za a baje kolin kayyaykin al’adu da suka
hada da abubuwan hannu da sauransu a wurin.
Bayanin ya ci gaba da cewam baya ga
shugaba Rauhani,akwai wadanda suke rufa masa daga cikinsu kuwa har da
mataimakin babbar cibiyar ta yada al’adun muslunci Mas’ud Sultani far, wanda
zai halarci tare da gabatar da bayani kan al’adun kasar ta Iran ga Faransawa da
suke da bukatar sanin wani abu kan hakan.
Daga cikin abubuwan da za a baje
kolinsu a wurin kuwa, har da kayan kida na zamanin da ya gabata, wanda
Iraniyawa suke amfani da s utu daruruwan shekaru, wadanda ake ajiyarsu a
matsayin wani abu na al’ada da ba za a manta da shi ba, wanda al’ummar Faransa
da dama suke nuna sha’arsu domin sanin wadannan ababe.
Daga karshe za a rufe taron tare da
gabatar da jawabai na hadin gwaiwa atsakanin
cibiyoyin yada al’adu na kasashen biyu, wadanda suke da tarihi na tsawon
shekaru, duk kwa da matsalolin da aka fuskanta daga bisani sakamakon batutuwa
na siyasa tsakanin Iran da kasashen turai.