Rasha Mubarak tana daga cikin masu kula da harkokin cibiyoyin musulmia wanann jaha ta bayyana cewa, a cikin 'yan shekarun baya-bayan nan an samu hare-hare a kan cibiyoyin musulmi da masallatansu da dama a cikin wannan jaha, kamar yadda kuma cin zarafi a kan daidaikun musulmi mazauna wannan jaha yake kara ta'azzara.
Bayanin cibiyar muuslmin ta vAmurka CAIR ya kara da cewa, sakamakon kamfe da dan takarar shugabancin kasar Amurka Donald Trump ke yi na kyamar musulmi, hakan ya kara ruruta wutar kyamar musulmia wannan jaha a baya-bayan nan.
Haka nan kuma bayanin ya kara da cewa akwai wasu kungiyoyi 33 a kasar masu adawa da musulmi, 3 daga cikinsu suna da mazaunin a jahar Florida, wanda hakan ya sanya cibiyar musulmin ta CAIR yin kira ga mahukunta musamman a wannan jaha da su dauki matakan da suka dace domin kare rayukan musulmi da dukiyoyinsu da kuma wuraren ibadarsu, kamar yadda dokar kasar ta tanada.