IQNA

Malamin Addini A Najeriya Ya Ce Maniyyata Su Rika Rubuta Wasiyya

23:45 - August 28, 2016
Lambar Labari: 3480751
Bangaren kasa da kasa, limamin Juma’a a birnin Abuja fadar mulkin tarayyar Najeriya ya bukaci maniyyata da su rika rubuta wasiyya kafin tafiya hajji.
Kamfanin dillanicn labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Daily Post cewa, Sheikh yahya Yalawi limamin masallacin Abuja ya bayyana cewa, yana da matukar muhimmanci maniyyata su rika rubuta wasiyya kafin tafiya aikin hajji.

Malamin ya ci gaba da cewa aikin hajji yana bukatar hakuri matuka, ta fskar gajiyar jiki, da bakunta, da wahalhalu da ke cikinsa, da kuma yadda mutum zai hadu da mutane da kasashen duniya da al’adu daban-daban.

Haka nan kuma ya yi ishara da abin da ya faru a shekarar da ta gabata, inda aka kasha alhazai dubbai lokacin gudanar da aikin hajji, lamarin da ya saka jama’a da dama yin shiri a lokacin tafiyarsu aikin hajjin bana, na wata kila su dawo, ko kuma basu dawo ba.

Najeriya dai na daga cikin kasashen da suka rasa alhazai da dama a lokacin aikin hajjin bara a lokacin jifar shedan a Mina, inda fiye da maniyantan kasar 270 suka riga mu gidan gaskiya.

Kamar yadda kuma limamin ya ja hankulan maniyyata da su tsarkake niyya ga Allah shi kadai a lokacin aikin hajji da sauran ayyuka na ibada, domin kuwa duk wanda ya yi wani aiki ba domin Allah ba, to bas hi da ladar wannan aikin a wajen Allah.

Dangane da guzuri kuma ya ja hankulan jama’a da su tabbatar da cewa sun guzuri ne da abin da yake daga halal, domin kuwa Allah madaukakin sarki mai tsarki ne baya karba sai mai tsarki.

3525816

Abubuwan Da Ya Shafa: kamfanin dillancin labaran
captcha