Ya ci gaba da cewa matsayin da kungiyarsu ta dauka na fatattakar 'yan ta'adda a cikin Lebanon da ma wasu wurare da suke barazana ga al'umma tana nan daram a kansa, domin yakin da kungiyar ke yi da 'yan ta'adda tana yin hakan ne a madadin sauran al'umma.
Haka nan kuma malamin ya yi tir da Allawadai da yadda kasashen da suka kafa wadannan kungiyoyi na 'yan ta'adda suke ci gaba da daukar nauyinsu domin kawai a rusa a kasashen musulmi, inda ya ce kasashen Amurka, da wasu an turawa gami da Turkiya da kuma Saudiyyah, su ne kan gaba wajen daukar nauyin dukkanin ayyukan ta'addancin da kungiyoyi irin su ISIS da sauran su suke aikatawa a cikin Iraki da Syria.
Ya ce a kan haka yaki da ta'adanci yana bukatar hakuri da juriya, domin kuwa duk wanda yake yaki da wadannan kungiyoyi na 'yan ta'adda, yana yaki ne kai tsaye da kasashen da aka ambata.