IQNA

Bam Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 6 A Birnin Bagadaza

20:40 - October 17, 2016
Lambar Labari: 3480861
Bangaren kasa da kasa, harin ta'addanci ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula biyu tare da jikkata wasu 6 na daban.
Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin press TV cewa, rahotani dake fitowa daga kasar Iraki sun tabbatar da tashin Bam a anguwar Kadisiya dake tsakiyar garin Bagdaza, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula biyu tare da jikkata wasu shida na daban.

A bangare guda Majiyar tsaron kasar ta sanar da cewa Jiragen yakin saman kasar sun kai hari a wuraren 'yan ta'addar IS dake yammacin garin Ramadi na jihar Anbar, lamarin da ya yi sanadiyar hallaka 'yan ta'adda 13 tare da lalata wasu daga cikin motocin su.

Wannan hari na zuwa ne a yayin da 'yan ta'addar ke kokarin kai wa Sojojin Irakin hari a kan hanyar su ta garin Biji zuwa Hadisa, lamarin da ya yi sanadiyar dakile ta'addancin.

A gefe guda Rundunar hadin gwiwar da aka kafa don 'yanto garin Mosil ta sanar da fara kai hare- hare kan 'yan ta'addar a birnin na Mosil.

Hakan yana zuwa ne a daidai lokacin da dakarun kasar Iraki suke shirin fara kaddamar da harin kwato birnin na Mausil daga ‘yan ta’addan takfiriyyah, lamarin ya harzuka kasashen da suke daukar nauyin ‘yan ta’addan.

3538106


captcha