Kamfanin
dillancin labaran kur’ani na iqn aya habarta cewa, ya nakalto daga shafin yanar
gizo na Dakar.icro cewa, taron zai yi dubi kan matsayin musulunci da mahangarsa
kan lamurra da suka shafi dniya a yau wanda kasashen Iran da Senegal suka dauki
nauyin shiryawa.
Taron dai wanda shi ne irinsa na farko, zai samu halartar masana daga kasashe 10, wadanda za su gabar laccoci tare da bayyana mahangarsu kan yadda ya kamata musulmi su fusknaci lamrran da suke wakana a duniya a halin yanzu.
Sheikh Bashir Mbaki babban daraktan cibiyar gudanar da tarukan addini na kasa da kasa a Senegal shi ne mai masafkin baki, inda sheikh Akhtari shugaban cibiyar Ahlul bait ta duniya yake a matsayin babban bako.