Bayann kwamitin wanda ma’aikatar kula da harkokin addini ta kasar ta amince da shi ya ce, cibiyar Azahar ce kawai take da hakkin ta nada malamai da suka dace su zama limaman manyan masallatai da za su rika yin huduba.
Sheikh Bakar Abdulhadi babban daraktan ma’aikatar kula da harkokin addini a lardin Dumyat ya bayyana cewa, akwai horo na musamman da cibiyar Azhar take bayarwa ga malamai, wanda ta akan ne ake bayar da izinin zama limamai masu huduba, ba kungiyar salafiyya ce take da hakkin yin haka ba.
Dangane da laarin da aka yada kan cewa shi ne da kansa ya bayar da sanarwar cewa yan salafiyya suna hakkin huduba da zabar limamai da kuma wa’azia acikin masallatai, malamin ya bayyana cewa babu gaskiya a cikin wannan zancen, domin shi kansa bas hi da hakkin yin hakan.