IQNA

Taron Tunawa Da Ranar Fara Limancin Imam Asr (AJ) A Hamburg

20:54 - December 08, 2016
Lambar Labari: 3481014
Bangaren kasa da kasa, a gobe ne za a gudanar da zaman taro na tunawa da ranar da Imam Hujja (AS) ya karbi limancin iyalan gidan manzon Allah.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na fa.izhamburg.de cewa, cibiyar muslunci da ke birnin Hamburg za ta shirya gudanar da wani zaman taro da misalign karfe 18:30 na dare, domin tunawa da ranar 9 ga watan rabiul Awwal wanda ya yi daidai da ranar da Imam Asr fara limanci.

Wannan taron dai zai samu halartar mabiya tafarkin iyalan gidan manzon Allah da suke zaune a birnin, kamar dai yadda aka saba yi a kowace shekara.

Ayatollah Ramezani babban daraktan cibiyar na daga cikin wadanda za su gabatar da jawabi a wurin kan wannan rana mai albarka da kuma matsayin ma'abucin ranar amincin Allah ya tabbata a gare shi.

Gobe ne 9 ga watan Rabiul awwal ranar da limancin limamin karshe na iyalan gidan manzon Allah ya fara, wanda kuma wannan ran ace mai matukar muhimamnci mabiya tafarkin iyalan gidan manzon Allaha duniya baki daya.

3552088


captcha