Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna
ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na fa.izhamburg.de cewa,
cibiyar muslunci da ke birnin Hamburg za ta shirya gudanar da wani zaman taro
da misalign karfe 18:30 na dare, domin tunawa da ranar 9 ga watan rabiul Awwal
wanda ya yi daidai da ranar da Imam Asr fara limanci.
Wannan taron dai zai samu halartar mabiya tafarkin iyalan gidan manzon Allah da suke zaune a birnin, kamar dai yadda aka saba yi a kowace shekara.
Ayatollah Ramezani babban daraktan cibiyar na daga cikin wadanda za su gabatar da jawabi a wurin kan wannan rana mai albarka da kuma matsayin ma'abucin ranar amincin Allah ya tabbata a gare shi.
Gobe ne 9 ga watan Rabiul awwal ranar da limancin limamin karshe na iyalan gidan manzon Allah ya fara, wanda kuma wannan ran ace mai matukar muhimamnci mabiya tafarkin iyalan gidan manzon Allaha duniya baki daya.