IQNA

Ministan Harkokin Addini A Masar Ya Ce Musulunci Ba Shi Da Alaka Da Ta'addanci

23:38 - June 15, 2017
Lambar Labari: 3481613
Bangaren kasa da kasa, Minista mai kula da harkokin addinin a kasar Masar ya mayar da kakkausar martani a kan masu danganta ayyukan ta'addanci da addinin muslunci.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Shafin jaridar yanar gizo ta Yaum Sabi ya bayar da rahoton cewa, Muhammad Mukhtar Juma'a minista mai kula da harkokin addini a kasar Masar ya bayyana cewa, danganta addinin musulunci da ayyukan ta'addanci da wasu masu dauke da akidar kafirta musulmi suke aikatawa, yin hakan babban kure ne.

Ministan ya ce addinin muslunci addini ne da ya zo domin kubutar da rayuwar dan adam da mutuncinsa, saboda haka duk wani abu na kisan dan adam ba gaira ba sabar ko zcin mutuncinsa baya da alaka da muslunci, ko da kuwa mai aikata hakan ya danganta kansa da musulunci.

A daya bangaren ministan ya kirayi malaman addini da cewa su sauke nauyin da ya rataya akansu na wayar da kan musulmi musamman matasa, wadanda su ne aka fi sauran kwasa a duk lokacin da wata guguwa ta zo, domin tabbatar da cewa sun iya banbance mene ne addinin muslunci da koyarwarsa, domin kada su fada cikin kungiyoyin ta'addanci da sunan suna addini.

3609725


captcha