IQNA

Isra'ila Na Ci Gaba Da Rufe Masallacin Aqsa In Ji Almanar

22:22 - July 16, 2017
Lambar Labari: 3481706
Isra'ila Na Ci Gaba Da Rufe Masallacin Aqsa In Ji Almanar
Bangaren kasa da kasa, Haramtacciyar kasar Isra'ila na ci gaba da rufe masallacin Aqsa tare da hana musulmi yin salla a cikinsa kwanaki uku a jere.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, tun bayan harin daukar fansa a kan jami'an tsaron yahudawan Isra'ila da wasu Palastinawa 'yan gwagwarmaya suka kai a kusa da kofar masallacin Quds a ranar Juma'a da ta gabata, har yanzu yahudawan na ci gaba da rufe masallacin mai alfarma.

Harin wanda ya yi sanadiyyar halakar 2 daga cikin sojojin yahudawa tare da yin shahadar maharan uku, ya girgiza haramtacciyar kasar Isra'ila matuka, inda take kallon hakan a matsayin wata manuniya kan cewa, Palastinawa sun fara daukar wasu sabbin matakai na daukar fansa kan kisan da ake yi musu a kullum rana ta Allah.

Kungiyoyin gwagwarmaya na Palastinawa da kuma wasu kasashen larabawa da suka hada da Lebanon, sun yi na'am da wannan harin daukar fansa a kan jami'an tsaron yahudawan Isra'ila.

3619260




Isra'ila Na Ci Gaba Da Rufe Masallacin Aqsa In Ji Almanar
captcha