IQNA

Wata Kungiyar Musulmi Ta Yi Allah Wadai Da Kai Hari Kan Coci A Najeriya

21:19 - August 07, 2017
Lambar Labari: 3481774
Bangaren kasa da kasa, wata kungiyar musulmi a Najeriya ta fitar da bayanin yin Allah wadai a kan kaddamar da hari a kan wata majami'ar mabiya addinin kirista a jahar Anambara.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin yada labarai na sunnewsonline cewa, a jiya wasu masu dauke da makamai sun kaddamar da hari a kan wata majami'a inda suka kasha mutane akalla 10 tare da jikkata wasu 18 na daban.

Ibrahim Abdullahi shi ne shugaban kungiyar, ya bayyana wannan hari da cewa na ta'addanci ne kuma na dabbanci, domin kuwa babu wani dalili da zai sanya dan adam ya kai haria kan wurin da mutane suke gudanar da ibada ta addininsu.

Ya ci gaba da cewa kungiyarsu wadda take sanya ido a kan lamurra da suka shafi musulmi a Najeriya tana yin Allah wadai da kakkausar muryka wannan mummunan aiki na kai hari a kan coci a kan mabiya addinin kirista.

A bangare guda kuma ya yi kira ga mahukunta da adauki matakin bincike domin gano wadanda suke da ahnnu a cikin wannan aika-aika domin hikunta a gaban kuliya, tare da daukar dukkanin matakan da suka dace domin kare rayukan 'yan Najeriya.

Haka na kuam ya yi kira ga sauran dukkanin mabiya addinai a kasar da su rungumi hakuri da zaman lafiya da juna tare da fahitar juna da kuma girmama ra'ayoyi da akidun junasu a matsayinsu na 'yan kasa guda.

3627847


captcha