IQNA

Tilasta Mabiya Mazhabar shi'a Fiyewa Daga Yankunansu A Awamiyyah

21:21 - August 07, 2017
Lambar Labari: 3481775
Bangaren kasa da kasa, jaridar middlieast ta bayar da rahoton cewa, jami'an masarautar Al Saud suna tilasta al'ummar yankin Awamiyya barin muhallansu.
Kamfanin dillancin labaran iqn aya habarta cewa, ya nakalto daga shafin hikima cewa, jaridar ta kasar Birtaniya ta habarta cewa, mahukuntan masarautar iyalan gidan Saud suna ci gaba da yin ruwan bama-bamai a kan al'ummar yankin Awamiyya tare ad tlasta su barin gidajensu.

Wannan mataki na zalunci da danniya na iyalan gidan saud ya zo a daidai lokacin da masarutar kasar ta dauki salon shelanta yaki a kan mabiya tafarkin ahlul bait a fadin gabas ta tsakiya.

An kasha mutane da dama tare da jikata wasu da kuma rusa daruruwan gidajen jama'a a yankin an Awamiyya, tare da wawushe dukiyoyin al'ummar yankin wadanda 'yan kasa ne kamar yadda Al Saud suke.

Al ummar gabashin saudiyya mabiya mazhabar shi'a ne wadanda mabiya adidar wahabiyanci suke tsananin gaba da su, wanda kuam masarautar 'ya'yan saud ta ginu ne kan akidar wahabiyanci da yaki da shi'a da kuma 'yan sunna da suke sabawa wannan akida.

Dukkanin arzikin danyen man fetur da iskar gas da Saudiyya ta dogara da shi ana fitar da shi ne daga yankuna 'yan shi'a da ke gabashin kasar, amma kuma ana haramta musu hakkokinsu a matsayinsu na 'yan kasa

3627624


captcha