Ya ci gaba da cewa hakika abin da ya faru lamari ne nab akin ciki, kuma majalisar dinkin duniya a shirye take ta bayar da dukkanin taimakon da ake bukata.
A daren jiya ne dai aka samu girgizar kasa wadda ta kai daraja 7.3 a ma'aunin ritche a Kermansha da ke Iran da kuma Sulamimaniyya a Iraki.
Haka nan kuma an ji motsin wannan girgizar kasa a kkasashen Turkiya, Armania, saudiyya, Kuwait da kuma hadaddiyar daular larabawa.