IQNA

Majalisar Dinkin Duniya Ta Mika Ta'aziyya Ga Iran Da Iraki Kan Girgizar Kasa

16:38 - November 13, 2017
Lambar Labari: 3482097
Bangaren kasa da kasa, majalisar dinkin duniya ta aike da sakon taya alhini ga al'umomin Iran da Iraki sakamakon girgizar kasar da aka yi wadda ta lashe rayukan daruruwan mutane.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na shafaq cewa, babban sakatare majalisar dinkin duniya ya aike ad sakon ta'aziyya zuwa ga gwamnatoci da al'ummomin Iraki da Iran, dangane da girgizar kasar da aka yi wadda ta lashe rayukan jama'a.

Ya ci gaba da cewa hakika abin da ya faru lamari ne nab akin ciki, kuma majalisar dinkin duniya a shirye take ta bayar da dukkanin taimakon da ake bukata.

A daren jiya ne dai aka samu girgizar kasa wadda ta kai daraja 7.3 a ma'aunin ritche a Kermansha da ke Iran da kuma Sulamimaniyya a Iraki.

Haka nan kuma an ji motsin wannan girgizar kasa a kkasashen Turkiya, Armania, saudiyya, Kuwait da kuma hadaddiyar daular larabawa.

3662740


captcha