Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, majiyoyin jami'an tsaro sun ce an yi dauki ba dadi tsakanin 'yan addinin Buda da kuma musulmi, a lokacin da musulmin suke kokarin kare masallacinsu daga farmakin 'yan Buda, lamarin da ya yi sanadiyyar jikkatar mutane da dama daga bangarorin biyu.
Tun da jimawa dai mabiya addinin Buda suna zargin cewa muuslmi suna neman su mamaye musu yanki, tare da kafa cibiyoyinsu da makarantu da kuma masallatai.
A cikin 'yan makonnin da suka gabata ma wani dan addinin Buda ya rasa ransa a wata hatsaniya tsakaninsa da sauran abokansa, amma kuma 'yan Buda sun dora alhakin mutuwarsa akan musulmi, inda suka kona gidaje fiye da 200 mallakin muuslmi, gami da shaguna da kuma masallatai guda 11.