IQNA

Zaman Gaggawa A MDD Kan Kisan Kiyashin Gaza

23:29 - June 09, 2018
Lambar Labari: 3482741
Bangaren kasa da kasa, majalisar dinkin duniya za ta gudanar da zaman gaggawa kan hare-haren baya-bayan nan da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar kan al’ummar Gaza.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, sakamakon kiran da wasu kasashen larabawa suka yi, babban zauren majalisar dinkin duniya zai gudanar da zaman gaggawa tare da halartar wakilan kasashe 193 kan hare-haren da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar kan al’ummar Gaza a baya-bayan nan.

Rayad Mansur wakilin Palastine a majalisar dinkin duniya shi ne ya gabatar da takardar neman a gudanar da wannan zama, ida ya ce abin da Isra’ila ta yi kan a’ummar Gaza abin yin Allawadai ne.

Ya kara da cewa, yana yin kira ga dukkanin kasashen duniya masu ‘yancin siyasa da su yi Allawadai da abin da Isra’ila take yi kan al’ummar Palastnu na kisan kiyashi musamman kan al’ummar Gaza marassa kariya.

3721120

 

 

 

 

 

 

 

captcha