IQNA

23:39 - September 26, 2018
Lambar Labari: 3483014

EU Ta Ce Rusa Khan Ahmar Laifin Yakin Isra'ila Ta Tafka

Tawagar 'yan kwamitin kula alakar da ke tsakanin kungiyar tarayyar Turai da Palasdinu a Majalisar Dokokin Kungiyar Tarayyar Turai ta bayyana cewa; Duk wani matakin rusa kauyen Khan Ahmar da ke gabashin birnin Qudus na Palasdinu yana matsayin laifin yaki ne.

EU Ta Ce Rusa Khan Ahmar Laifin Yakin Isra'ila Ta Tafka

Kamfanin dillancin labaran iqna, 

A ziyarar gani da ido da tawagar 'yan kwamitin kula da alakar da ke tsakanin kungiyar tarayyar Turai da Palasdinu a Majalisar Dokokin Kungiyar Tarayyar Turai ta kai zuwa kauyen Khan Ahmar da ke dauke da Palasdinawa da masu rajin kare hakkin bil-Adama na kasa da kasa da suke goyon bayan al'ummar Palasdinu a jiya Laraba.

Tawagar 'yan Majalisun Dokokin Kungiyar ta Tarayyar Turai ta jaddada cewa: Duk wani matakin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila zata dauka na rusa kauyen, yana matsayin laifin yaki ne.

Tun a ranar 12 ga wannan wata na Satumba ne kotun kolin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila ta bada izini ga sojojin haramtacciyar kasar Isra'ila kan rusa kauyen na Khun Ahmar a cikin mako guda.

Kauyen Khan Ahmar dai yana dauke ne da Palasdinawa 'yan gudun hijira da aka raba su da muhallinsu tun a shekara ta 1953, kuma a halin yanzu kauyen yana matsayin sansanin gudanar da zaman dirshen domin nuna rashin amincewa da bakar siyasar gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila kan al'ummar Palasdinu.  

3750461

 

captcha