IQNA

An Hana Tawagar Isra'ila Shiga Tunisia

22:57 - November 03, 2018
Lambar Labari: 3483096
An Hana Tawagar Isra'ila Shiga Tunisia
Bangaren kasa da kasa, Kotun birnin Tunis fadar mulkin kasar Tunisia ta yanke hukuncin haramta wa wata tawagar Isra'ila shiga kasar, domin halartar wani taro kan addinai da za a gudanar a kasar.

Kamfanin  dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Shafin jaridar Al-shuruq ta kasar Tunisia ya bayar da rahoton cewa, sakamakon kararrakin da kungiyoyin da ke fafutukar kare hakkokin falastinawa a kasar Tunisia, domin hana tawagar Isra'ila halartar wani taron addinai da za a gudanar a kasar, kotun ta yanke hukuncinta na karshe, inda ta haramta shigowar tawagar Isra'ila a cikin kasar domin halartar taron.

Kungiyoyin sun dauki wannan matakin ne domin nuna rashin amincewarsu da abin da Isra'ila take na kisan gilla a kan al'ummar Falastinu, ba tare da duniya ta damu da hakan ba, yayin da kuma a lokaci guda ma wasu daga cikin kasashen larabawan yankin gabas ta tsakiya, suke ta hankoron ganin sun kulla alaka da Isra'ila.

A ranar 8 ga wannan wata na Nuwamba ne za a fara gudanar da taron mabiya addinai na duniya a birnin Tunis na kasar Tunisia, wanda zai samu halartar wakilai daga kasashen duniya daban-daban.

3760942

 

 

 

 

 

 

captcha