IQNA

Sabon Shirin Hana Kiran Salla A Quds

22:52 - January 04, 2019
Lambar Labari: 3483282
Gwamnatin Isra'ila tana shirin fara aiwatar da wani shiri na musamman domin hana Falastinawa yin kiran salla a masallatai.

Kamfanin dilancin labarai na iqna, Shafin yada labarai na Quds Press ya bayar da rahoton cewa, Isra'ila na shirin daukar wasu sabbin matakai na hana yin kiran sala a masallatan Falastinawa da suke kusa da matsugunnan yahudawa a birnin Quds.

Rahoton ya ce, matsugunnan yahudawan da aka gina  a cikin yankunan Falastinawa na yankunan Bait Safafa, bait Hanina, da kuam Bait Makbir, wadanda dukakninsu suke a yankunan gabashin birnin Quds.

Shirin ya hada da baiwa 'yan sandan yahudawa damar shiga kowane masallaci suka ji a ana kiran salla, da su shiga su cire lasifikokin kuma su kashe wutar masallacin.

Tun a cikin shekarar da ta gabata ce dai Isra'ila ta kafa dokar hana yin kiran salla a yankunan Falastinawa da suke a kusa da matsugunnan yahudawa 'yan share wuri zauna, amma Falastinawa sun yi wasti da wannan doka, inda suke ci gaba da yin kiran salla a masallatai a duk lokutan salloli guda biyar, lamarin da yake bakanta ran yahudawan da ke a cikin yankunan.

3777922

 

captcha