IQNA

Zarif Ya Ce Akwai Shakku Dangane Da Manufar Kai Hari Kan Jiragen Daukar Mai

23:56 - June 13, 2019
Lambar Labari: 3483734
Zarif Ya Ce Akwai Shakku Dangane Da Manufar Kai Hari Kan Jiragen Daukar Mai
Ministan harkokin wajen kasar Iran Muhammad Jawad Zarif ya bayyana cewa akwai shakku matuka dangane da harin da aka kai yau a kan jiragen dakon mai a tekun Oman.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a yau ministan harkokin wajen kasar Iran Muhammad Jawad Zarif ya bayyana a shafinsa na twitter cewa, akwai shakku matuka dangane da harin da aka kai yau a kan  jiragen dakon mai a tekun Oman da kuma manufar yin hakan.

Ya ce an kai wadannan hae-hare ne a daidai lokacin da frayi ministan Japan yake ganawa da jagoran juyin juya halin muslunci a Iran, wanda kuma manufar ziyarar asa ita c yadda za a samar da hanyoyin zaman lafiya a yankin.

 

3819138

 

captcha