IQNA

Taron Tunawa Da Ranar Wafatin Manzon Allah (SAW) A Landan

23:33 - October 25, 2019
Lambar Labari: 3484189
A ranar Lahadi mai zuwa za a gudanar da taron tunawa da ranar wafatin manzon Allah (SAW) da shahadar Imam Hassan (AS).

Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, cibiyar musuunci ta birnin Lanadan ta sanar da cewa, a ranar Lahadi mai zuwa za a gudanar da taron tunawa da ranar wafatin manzon Allah da shahadar Imam Hassan wanda yay i daida da ranar 28 ga watan Safar, inda Sayyid Hashem Musawi zai gabatar da jawabai.

Za a fara taron na tunawa da ranar wafatin manzon Allah (SAW) da shahadar Imam Hassan (AS) zai gudana ne daga misalign karfe 19:45 na yammacin ranar ta Lahadi.

Haka nan kuma wannan cibiyar za ta gudanar da wani zaman taron na tunawa da zagayowar ranar shahada Imam Rida (AS) a babban ginin cibiyar da misalign karfe 19:45 na dare 30 ga watan Safar.

 

3852148

 

 

 

captcha