Kamfanin dillancin labaran IQNA, a yau Sayyid Abbas Musawi kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya fadi cewa, maimakon nuna goyon baya ga mabarnata a Iran, da zai fi kyau ga kasashen turai su cika alkawullan da su ka daukarwa Iran.
Ya ce abin da turawa suke nunawa kan goyon bayan masu zanga-zanga da barnata kaddrorin gwamnati da na jama’a da bankawa gidajen mai wuta da motocin bas bas masu daukar jama’a, hakan ya yi kama da munafunci.
Ya kara da cewa maimakon hakan da zai fi kyau su aiwatar da dukkanin abubuwan da suka yi alkawali a cikin ayrjejeniyar da suka cimmawa da Iran, wanda har yanzu ba su aiwatar ba.