IQNA

23:50 - March 01, 2020
Lambar Labari: 3484574

Gasar Kur’ani Ta Kasa Da Kasa A Masar A Daidai Lokacin Da Ake Tsoron Yaduwar Corona

Tehran (IQNA) mahkunta a kasar Maar sun sanar da cewa duk da barazanar yaduwar cutar corona a duniya za a gudanar da gasar kur’ani ta duniya a kasar.

Gasar Kur’ani Ta Kasa Da Kasa A Masar A Daidai Lokacin Da Ake Tsoron Yaduwar Corona

Shafin yada labarai na Yaum Sabi ya bayar da rahoto ewa, Adel Gadban gwamnan lardin Port Said na kasar Masar ya bayyana cewa, an kammala dukkanin shirye-shirye na gudanar da gasar kur’ani ta duniya a wannan lardi, tare da halartar kasashe 40 na duniya.

Ya ce babban abin alfahari gare su kan yadda wannan gasa take gudana a karo na uku kenan a cikin lardin Port Sa’id, inda ya ce a shekarar bana ma da yardarm Allah gasar za ta fara gudana a karshen wannan mako.

Gasar dai tana samun halartar manyan jami’an gwamnati da kuam malamai daban-daban daga sassa na kasar ta Masar, gami da wakilan kasashen duniya.

Khaled Mujahid kakakin ma;aikatar kiwon lafiya na kasar Masar yak ore labarin da ke cewa akwai mutane 6 a kasar ad suke dauke ad cutar corona.

Ma’aikatr kiwon lafiya ta Masar ta bayyana cewa, mutum daya ne aka samu da cutar a kwanakin baya, kuma  ahalin yanzu ya warke tangaram babu kwayoyin cutar tare da shi.

 

3882239

 

 

 

 

captcha