Wannan bayani na jagora ya zo ne a shafinsa na twitter inda ya yi Allah wadai da kisan da mabiya addinin Hinbdu suke yi wa Musulman kasar India wanda adadinsu ya kai arbai’in a cikin kwanaki hudu da suka gabata.
Haka nan kuma ya kuma bukaci gwamnatin kasar Indiya ta hana mabiya addinin Hindu masu tsatsauran ra’ayin addini fada wa Musulman kasar.
Sannan kuma ya bayyna cewa zukatan musulmi suna kuna matuka saboda ganin yadda ake yi wa musulman kasar india kisan kiyashi.
Ko a kwanaki uku da suka gabata ma ministan harkokin wajen kasar Iran ya yi kira ga gwamnatin kasar ta Indiya da ta hada kan mutanen kasar ta kuma daina nuna bambanci a cikin mabiya addinai na kasar da suke rayuwa tare da juna.