IQNA

Tarayyar Turai Ta Kirayi Isra'ila Ta Janye Shirin Mamayar Yankunan Falastinawa

22:48 - May 20, 2020
Lambar Labari: 3484820
Tehran (IQNA) Kungiyar tarayyar turai ta sanar da cimma matsaya kan yin watsi da shirin Isra’ila na mamaye yankunan Falastinawa da ke gabar yamma da kogin Jordan.

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya bayar da rahoton cewa, babban jami’I mai kula da harkokin siyasar wajen kungiyar tarayyar tarayyar turai Josep Borrell ya bayyana cewa, kasashen kungiyar tarayyar turai 25 daga cikin 27 sun cimma matsaya kan yin watsi da shirin da Isra’ila take da shi na mamaye sauran yankunan Falastinawa da ke yammacin kogin Jordan.

Ya ci gaba da cewa, kasantuwar wannan mataki na Isra’ila ya yi hannun riga da dukkanin dokoki na kasa da kasa, wannan yasa ala tilas kasahen tarayyar turai su yi watsi da hakan, kuma idan Isra’ila ta dage kan aiwatar da shirin nata na mamaye sauran yankunan Falastinawa da ke yammacin kogin Jordan, akwai yiwuwar tarayyar turai ta kakaba mata takunkumi.

Gwamnatin kwarya-kwaryan cin gishin kai ta Falastinawa, tare da bangarori daban-daban a Falastinu, sun lale marhabin da matakin na kungiyar tarayyar turai, tare da kiran wasu daga cikin kasashen larabawa da su koyi da hakan.

 

 

 

captcha