IQNA

Hudubar Juma’a Kai Tsaye A Gidan talabijin Na Uganda

22:51 - June 15, 2020
Lambar Labari: 3484896
Tehran (IQNA) gidan taabijin din gwamnatin kasar Uganda na watsa hudubar Juma’a kai tsaye da ake karantowa a kowace Juma’a.

Gidan talabijin din na Uganda yana watsa hudubar ne sakamakon dakatar da gudanar da sallolin Juma’a da aka saboda dakile yaduwar cutar corona.

Sheikh Sulaiman Kasule ne yake gabatar da hudubar daga gidansa ana dauka ana watsawa domin amfanin musulmi.

Musulmin kasar Uganda na daga cikin musulmin da ake buga misali da sua  bangarori daban-daban, da hakan ya hada da yadda suke rayuwa cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya tsakaninsu da ambiya addinin kirista.

Kasar Uganda da ke gabashin nahiyar Afirka, mafin yawan mutanenta mabiya addinin kirista ne, amma kuma suna zaman lafiya tare da musulmi, kamar yadda kuma suke girmama junansu.

 

3904992

 

captcha