IQNA

Amurka Ta Kakaba Wa Ministocin Lebanon takunkumi Saboda Hizbullah

22:48 - September 10, 2020
Lambar Labari: 3485170
Tehran (IQNA) Amurka ta kakaba wa wasu tsoffin ministocin kasar Lebanon takunkumi saboda alakarsu da kungiyar Hizbullah.

Amurka ta sanar da kababa wa ministocin biyu da suka fito daga kungiyar Amal da kuma kungiyar Maradah ta kiristoci, bisa zarginsu da cewa suna da kyakkyawar alaka da kungiyar Hizbullah.

Amurka ta bayyana cewa, ministocin biyu sun rika kare manufofin kungiyar Hizbullah a cikin gwamnati da kuma majalisar dokokin kasar Lebanon, a kan haka takunkumin da Amurka ta kakaba wa Hizbullah ya hada har da su a halin yanzu.

Kungiyar Hizbullah dai tana amatsayin wani bababn gishiki a cikin harkokin siyasar Lebanon, kamar yadda kuma mayakan kungiyar ne suka kawo karshen mamayar Isra’ila a kan kasar Lebanon a shekara ta 2000, kamar yadda kuma shakku kan irin martanin da kungiyar za ta mayar ne, ke hana Isra’ila aiwatar da duk wani kudirinta na mamaye wasu yankuna a kasar Lebanon.

3922046

 

captcha