IQNA

Alaka Na Kara Karfafa tsakanin Iran Da Iraki A Bangaren Tsaro

22:52 - November 15, 2020
Lambar Labari: 3485368
Gwamnatin kasar Iraki ta bayyana cewa ba ta tababa a kan sayen makamai kai tsaye daga kasar Iran.

Ministan tsaron kasar Iraki Juma’a Inad Sa’adun ne ya bayyana hakan a yau a lokacin da yake ganawa da babban hafsan hafsoshin soji na kasar Iran janar Muhammad Baqiri a birnin Tehran.

A yayin da yake tarbar ministan tsaron kasar Iraki a yau, babban hafsan hafsoshin sojin kasar Iran janar Baqiri ya bayyana cewa, kasahen biyu sun himmatu matuka wajen karfafa dangantakarsu ta tsaro, sakamakon barazanar da suke fuskanta.

Ya ce babu wani abu shamaki a lakar Iran da Iraki a dukkanin bangarori, da hakan ya hada har da bangaren tsaro, wanda sun yi nisa wajen fadada ayyukansu na hadin gwiwa a wannan fage.

Shi ma a nasa bangaren ministan tsaron kasar Iraki Inda Sa’adun ya jaddada cewa, babu gudu babu ja da baya wajen ci gab ada gudanar da ayyukan tsaro na hadin gwiwa  adukkanin bangarori tsakanin Iran da Iraki, kuma Iraki ba ta shayin kowa dangane da shirinta na sayen makamai daga kasar Iran.

Ziyarar ministan tsaron kasar Irakia  Iran dai na zuwa ne ‘yn makonni bayan dauke wa Iran takunkumin saye da sayar da makamai.

3935341

 

 

Abubuwan Da Ya Shafa: ministan tsaro kasar iraki iran wannan fage
captcha