IQNA

Sakon Jagora Kan Kisan Fitaccen Masanin Nukiliya Na Iran:

A Binciko Masu Hannu A Kisan Fakhrizadeh Kuma A Ci Gaba Da Bunkasa Tafarkinsa Na Ilimi

16:09 - November 28, 2020
Lambar Labari: 3485408
Tehran (IQNA) jagoran juyin juya halin mulsunci a Iran Ayatollah Sayyid Ali Khamenei ya fitar da sako dangane da kisan gillar da aka yi wa fitaccen masanin ilimin nukiliya na kasar a Jiya.

Jagoran juyin juya halin mulsunci a Iran Ayatollah Sayyid Ali Khamenei ya fitar da sako a yau dangane da kisan da aka yi wa babban masanin ilimin nukiliya na kasar Iran Mohsen Fakhrizadeh.

Matanin Sakon Jagora:

 

Da Sunan Allah Mai Rahma Mai Jin Kai

Fitaccen masani kan harkokin na ilimin nukiliya da kuma tsaro Malam Mohsen Fakhrizadeh ya yi shahada a hannun ‘yan kwangila masu kekasassar zuciya.

Hakika shi mutum ne da ya kasance mai kokari matuka, da himma maras tamka a cikin rayuwarsa, domin ganin ya yi hidima ga addinin Allah da kuma bayanin Allah, saboda haka yin shahada da ya yi wata babbar kyauta ce ya samu daga Allah.

Akwai abubuwa guda biyu da ya zama wajibi a mayar da hankalia  kansu bayan kisan gillar da aka yi masa, na daya a bi diddigin lamarin domin gano dukkanin wadanda suke da hannu a kisansa, da kuma wadanda suka sanya su, kuma a dauki matakin da ya dace a kansu.

Na biyu kuma a ci gaba da kara bunkasa ayyuka na ilimi a fagen da yake yake bayar da gudunmawa, a  bangaren nukiliya da sauran bangarori na tsaron kasa.

Daga karshe ina mika sakon ta’aziyya ga iyalansa, da kuma sauran abokan aikinsa a dukkanin bangarori.

 

Sayyid Ali Khamenei

28/11/2020

 

3937799

 

captcha