IQNA

Karatun Kur’ani Mauritania Domin Neman Allah ya Kawo karshen Korona

23:01 - December 13, 2020
Lambar Labari: 3485456
Tehran (IQNA) gwamnatin kasar Mauritania ta bullo da shirin karatun kur’ani domin rokon Allah ya kawo karshen korona.

Shafin yada labarai na Misr Yaum ya bayar da rahoton cewa, gwamnatin kasar Mauritania ta bullo da shirin karatun kur’ani domin rokon Allah ya kawo karshen cutar corona, wanda za a rika gudanarwa a wurare daban-daban.

Baya ga haka kuma za a rika saka karatun kur’ani a cibiyoyi na addini da masallatai a lokuta daban-daban, domin samun albarkar kur’ani mai tsarki wajen kawo karshen wannan annoba da ta addabi duniya.

Minista mai kula da harkoki addini na kasar Mauritania ya sanar da cewa, za a fara wannan shiri daga yau, kuma dukkanin limamai na kasar an sanar das u dangane wannan shiri.

Baya ga haka kuma gwamnatin Mauritania ta bukaci a ci gaba da kara kiyaye ka’idoji da dokoki na kiwon lafiya da jami’an kiwon lafiya suke fada  domin kaucewa kamuwa da wannan cuta.

 

3940785

 

Abubuwan Da Ya Shafa: kiyaye
captcha