Tashar RT ta bayar da rahoton cewa, a wani jawabi da ya yi kafin barin birnin Washington a yau, tsohon shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce zai sake dawowa fadar white house a wani lokaci a nan gaba.
A lokacin da yake gabatar da jawabin a gaban wasu magoya bayansa da suka hada da wasu daga cikin jami’an gwamnatinsa, Trump ya bayyana cewa ya samu nasarori masu tarin yawa a cikin shekaru hudu da ya yi yana mulkin Amurka.
Ya ce daga cikin nasarorinsa har da samar da rigakafin cutar corona, bayan nan kuma ya ce a lokacinsa ne aka samu karuwar ma’ikata a kasar, inda ba domin matsalolin corona ba, da an kara samun babban ci gaba a wannan bangare.
Dangane da batun zabe kuwa, ya bayyana cewa ya samu gagarumar nasara, domin kuwa a cewarsa ya samu kuri’u wajen miliyan 75 a zaben da aka gudanar a kasar.
Trump dai ya fice daga fadar white house da jijjifin safiyar yau, bayan fitar da wasu daga cikin kayayyakinsa da aka loda masa a jirgi, ya kuma bar birnin Washington kafin a rantsar da sabon shugaban kasar ta Amurka Joe Biden a yau, inda ya nufi jihar Florida.